6
Isra’ila marar tuba
“Ku zo, mu koma ga Ubangiji.
Ya yayyage mu kucu-kucu
amma zai warkar da mu;
ya ji mana ciwo
amma zai daure mana miyakunmu.
Bayan kwana biyu zai rayar da mu,
a rana ta uku zai tashe mu,
don mu rayu a gabansa.
Bari mu yarda da Ubangiji;
bari mu nace gaba don mu yarda da shi.
Muddin rana tana fitowa,
zai bayyana;
zai zo mana kamar ruwan bazara,
kamar ruwan saman farko da yake jiƙe ƙasa.”
 
“Me zan yi da kai Efraim?
Me zan yi da kai Yahuda?
Ƙaunarku tana kamar hazon safiya,
kamar raɓar safiya da takan ɓace.
Saboda haka na yayyaga ku kucu-kucu tare da annabawana,
na kashe ku da kalmomin bakina;
hukuntaina sun haskaka kamar walƙiya a kanku.
Gama jinƙai nake bukata, ba hadaya ba,
ku kuma san Allah a maimakon hadayun ƙonawa.
Kamar Adamu, sun tā da alkawari,
sun yi mini rashin aminci a can.
Gileyad birni ce ta mugayen mutane,
da tabon alamun jini.
Kamar yadda mafasa sukan yi fakon mutum,
haka ƙungiyoyin firistoci suke;
suna kisa a hanya zuwa Shekem,
suna aikata laifofi bankunya.
10 Na ga wani abu mai bantsoro
a gidan Isra’ila.
A can Efraim ya miƙa wuya ga karuwanci
Isra’ila kuma ta ƙazantu.
 
11 “Ku kuma, ya mutanen Yahuda,
na shirya muku ranar girbi.
 
“A duk sa’ad da zan mayar da dukiya wa mutanena,