2 Sama’ila
1
Dawuda ya ji labarin mutuwar Shawulu
Bayan mutuwar Shawulu, Dawuda ya dawo daga karkashe Amalekawa. Sai ya zauna a Ziklag kwana biyu. A rana ta uku sai ga wani mutum ya zo daga sansanin Shawulu da yagaggen riga da ƙura a kansa. Da ya zo wurin Dawuda sai ya fāɗi a ƙasa don yă nuna bangirma.
Dawuda ya tambaye shi ya ce, “Daga ina ka fito?”
Ya amsa ya ce, “Na tsere ne daga sansanin Isra’ila.”
Dawuda ya ce, “Gaya mini, me ya faru?”
Sai ya ce, “Mutane sun gudu daga yaƙi, aka kuma karkashe yawancin mutane. Shawulu da ɗansa Yonatan ma sun mutu.”
Sai Dawuda ya ce wa saurayin da ya kawo labarin, “Yaya ka san cewa Shawulu da ɗansa Yonatan sun mutu?”
Saurayin ya ce, “Ina kan dutsen Gilbowa a lokacin sai na ga Shawulu jingine a māshinsa. Kekunan yaƙi da mahayansu suna matsowa kusa da shi. Da ya juya ya gan ni sai ya kira ni, na kuwa ce masa, ‘Ga ni?’
“Ya tambaye ni ya ce, ‘Wane ne kai?’
“Na ce, ‘Ni mutumin Amalek ne.’
“Sai ya ce mini, ‘Matso kusa ka kashe ni! Ina cikin azabar mutuwa, sai dai har yanzu ina da rai.’
10 “Saboda haka na matso kusa da shi na kashe shi, domin na san cewa ba zai yi rai ba, da yake ya riga ya fāɗi. Sai na cire rawanin da yake kansa, na kuma cire warwaron hannunsa, na kuwa kawo maka su duka, ranka yă daɗe!”
11 Sai Dawuda da dukan mutanen da suke tare da shi suka yayyage rigunarsu. 12 Suka yi makoki, da kuka, da azumi har yamma saboda Shawulu da ɗansa Yonatan, da saboda sojojin Ubangiji, da kuma gidan Isra’ila, gama an karkashe su a yaƙi.
13 Dawuda ya ce wa saurayin da ya kawo labarin, “Daga ina ka fito?”
Ya ce, “Ni ɗan wani baƙo ne, mutumin Amalek.”
14 Dawuda ya ce masa, “Yaya ba ka ji tsoro ɗaga hannu ka hallaka shafaffe na Ubangiji ba?”
15 Sai Dawuda ya kira ɗaya daga cikin mutanensa ya ce, “Je ka kashe shi!” Haka kuwa ya buge shi, ya kuwa mutu. 16 Gama Dawuda ya riga ya ce masa, “Alhakin jininka yana bisa kanka tun da yake da bakinka ka ce, ‘Ni ne na kashe shafaffe na Ubangiji.’ ”
Dawuda ya yi makokin Shawulu da Yonatan
17 Dawuda ya rera wannan makoki saboda Shawulu da ɗansa Yonatan. 18 Ya umarta a koya wa mutanen Yahuda wannan waƙa mai suna Makokin Baka (tana a rubuce a Littafin Yashar),
19 “Ya Isra’ila, an kashe darajarki a kan tuddanki.
Ga shi, jarumawa sun fāɗi!
 
20 “Kada a faɗe shi a Gat,
kada a yi shelarsa a titunan Ashkelon,
don kada ’yan matan Filistiyawa su yi murna
don kada ’yan matan marasa kaciya su yi farin ciki.
 
21 “Ya duwatsun Gilbowa,
kada a sāke yin ruwa ko raɓa a kanku,
balle gonakin da suke ba da hatsin hadaya su ƙara bayarwa.
Gama a can ne garkuwoyin manyan sojoji suka kwanta,
suka kwanta a wulaƙance.
Garkuwar Shawulu kuwa,
ba za a ƙara shafa mata mai ba.
 
22 “Daga jinin waɗanda aka kashe,
daga tsokar naman jarumi,
bakan Yonatan bai juye baya ba,
takobin Shawulu bai komo ba tare da gamsuwa ba.
23 Shawulu da Yonatan,
a raye ƙaunatattu ne da kuma bansha’awa,
a mace kuma ba su rabu ba.
Sun fi gaggafa sauri,
sun fi zaki ƙarfi.
 
24 “Ya ku ’yan matan Isra’ila,
ku yi kuka saboda Shawulu,
wanda ya suturta ku da jajjayen kayan ado,
wanda ya yi wa rigunarku ado da zinariya.
 
25 “Jarumawa sun fāɗi a yaƙi!
Ga Yonatan matacce a tuddanku.
26 Na yi baƙin ciki saboda kai, Yonatan ɗan’uwana;
ƙaunatacce kake a gare ni.
Ƙaunarka a gare ni abar al’ajabi ce,
abar al’ajabi fiye da ta mace.
 
27 “Jarumawa sun fāɗi!
Makaman yaƙi sun hallaka!”