Zabura 64
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. 
 
1 Ka ji ni, ya Allah, yayinda nake faɗin abin da yake damuna;  
ka tsare raina daga barazanan abokin gāba.   
   
 
2 Ka ɓoye ni daga ƙulle-ƙullen mugaye,  
daga daure dauren wannan taro masu aikata mugunta.   
3 Sukan wāsa harsunansu kamar takuba  
su harba kalmominsu kamar kibiyoyi masu kisa.   
4 Sukan yin kwanto su harbi marar laifi;  
sukan yi harbi nan da nan, ba tsoro.   
   
 
5 Sukan ƙarfafa juna a mugayen ƙulle-ƙullensu,  
sukan yi magana yadda za su ɓoye tarkunansu;  
su ce, “Wa zai gan su?”   
6 Sukan yi ƙulle-ƙullen rashin adalci su ce,  
“Mun gama ƙulla cikakkiyar maƙarƙashiya tsab!”  
Zuciyar mutum da tunaninsa, suna da wuyar ganewa.   
   
 
7 Amma Allah zai harbe su da kibiyoyi;  
nan da nan za a buge su su fāɗi.   
8 Zai juya harshensu a kansu  
yă kuma kawo su ga hallaka;  
duk waɗanda suka gan su za su kaɗa kai, suna musu ba’a.   
9 Dukan mutane za su ji tsoro;  
za su yi shelar ayyukan Allah  
su kuma yi tunanin abin da ya aikata.   
   
 
10 Bari masu adalci su yi farin ciki a cikin Ubangiji  
su kuma nemi mafaka a gare shi;  
bari dukan masu gaskiya a zuciya su yabe shi!