Zabura 101
Ta Dawuda. Zabura ce. 
 
1 Zan rera wa ƙauna da adalcinka;  
gare ka, ya Ubangiji, zan rera yabo.   
2 Zan yi hankali ga yin rayuwa marar zargi,  
yaushe za ka zo gare ni?  
   
 
Zan bi da sha’anin gidana  
da zuciya marar abin zargi   
3 Ba zan kafa a gaban idanuna 1  
wani abu marar kyau ba.  
   
 
Na ƙi jinin ayyukan mutane marasa aminci;  
ba za su manne mini ba.   
4 Mutane masu mugun zuciya za su nesa da ni;  
ba abin da zai haɗa ni da mugunta.   
   
 
5 Duk wanda ya yi ɓatanci wa maƙwabcinsa a ɓoye  
shi za a kashe;  
duk mai renin wayo da mai girman kai,  
ba zan jure masa ba.   
   
 
6 Idanuna za su kasance a kan amintattu a cikin ƙasar,  
don su zauna tare da ni;  
tafiyarsa ba ta da zargi  
zai yi mini hidima.   
   
 
7 Babu mai ruɗun  
da zai zauna a gidana;  
babu mai ƙaryan  
da zai tsaya a gabana.   
   
 
8 Kowace safiya zan rufe bakunan  
dukan mugaye a ƙasar;  
zan yanke kowane mai aikata mugunta  
daga birnin Ubangiji.