22
Misalin bikin aure
(Luka 14.15-24)
Yesu ya sāke yin musu magana da misalai, yana cewa, “Mulkin sama yana kama da wani sarki wanda ya shirya bikin auren ɗansa. Sai ya aiki bayinsa su kira waɗanda aka gayyata zuwa bikin, amma waɗanda aka ce su zo bikin, suka ƙi zuwa.
“Sai ya sāke aiken waɗansu bayi ya ce, ‘Ku ce wa waɗanda aka gayyata cewa na shirya abinci. An yanka bijimai da shanun da aka yi kiwo, kome a shirye yake. Ku zo bikin auren mana.’
“Amma ba su kula ba, suka kama gabansu, ɗaya ya tafi gonarsa, ɗaya kuma ya tafi kasuwancinsa. Sauran suka kama bayinsa suka wulaƙanta su, suka kuma kashe su. Sai sarkin ya yi fushi. Ya aiki mayaƙansa suka karkashe masu kisankan nan, aka kuma ƙone birninsu.
“Sa’an nan ya ce wa bayinsa, ‘Bikin aure fa ya shiryu, sai dai mutanen da na gayyata ba su dace ba. Ku bi titi-titi ku gayyato duk waɗanda kuka gani, su zo bikin.’ 10  Saboda haka bayin suka bi titi-titi, suka tattaro duk mutanen da suka samu, masu kirki da marasa kirki, zauren bikin ya cika makil da baƙi.
11  “Amma da sarkin ya shigo don yă ga baƙin, sai ya ga wani can da ba ya sanye da kayan auren. 12  Ya yi tambaya ya ce, ‘Aboki, yaya ka shigo nan ba tare da rigar aure ba?’ Mutumin ya rasa ta cewa.
13  “Sai sarkin ya ce wa fadawa, ‘Ku daure shi hannu da ƙafa, ku jefar da shi waje, cikin duhu, inda za a yi kuka da cizon haƙora.’
14  “Gama kirayayu da yawa, amma zaɓaɓɓu kaɗan ne zaɓaɓɓu.”
Biyan haraji ga Kaisar
(Markus 12.13-17; Luka 20.20-26)
15 Sai Farisiyawa suka yi waje, suka ƙulla yadda za su yi masa tarko cikin maganarsa. 16 Suka aiki almajiransu tare da mutanen Hiridus wurinsa. Suka ce, “Malam, mun san kai mutum ne mai mutunci, kuma kana koyar da maganar Allah bisa gaskiya. Mutane ba sa ɗaukan hankalinka, domin ba ka kula ko su wane ne ba. 17 To, ka gaya mana, a ra’ayinka? Ya dace a biya Kaisar haraji ko a’a?”
18 Amma Yesu da yake ya san mugun nufinsu, sai ya ce, “Ku munafukai, don me kuke ƙoƙarin sa mini tarko? 19  Ku nuna mini kuɗin da ake biyan haraji da shi.” Sai suka kawo masa dinari, 20 sai ya tambaye su ya ce, “Hoton wane ne wannan? Kuma rubutun wane ne?”
21 Suka amsa, “Na Kaisar ne.”
Sai ya ce musu, “Ku ba wa Kaisar abin da yake na Kaisar, ku kuma ba wa Allah abin da yake na Allah.”
22 Da suka ji haka, sai suka yi mamaki. Saboda haka suka ƙyale shi, suka yi tafiyarsu.
Aure a tashin matattu
(Markus 12.18-27; Luka 20.27-40)
23 A ranan nan Sadukiyawa, waɗanda suke cewa babu tashin matattu, suka zo wurinsa da tambaya. 24 Suka ce “Malam, Musa ya faɗa mana cewa in mutum ya mutu ba shi da ’ya’ya, dole ɗan’uwansa yă auri gwauruwar yă kuma haifar wa ɗan’uwan ’ya’ya. 25 A cikinmu an yi ’yan’uwa guda bakwai. Na fari ya yi aure, ya mutu, da yake bai sami ’ya’ya ba, sai ya bar matarsa wa ɗan’uwansa. 26 Haka ya faru da ɗan’uwa na biyu da na uku, har zuwa na bakwai. 27 A ƙarshe, macen ta mutu. 28 To, a tashin matattu, matar wa a cikinsu bakwai ɗin nan za tă zama, da yake dukansu sun aure ta?”
29 Yesu ya amsa ya ce, “Kun ɓata, domin ba ku san Nassi ko ikon Allah ba. 30  Ai, a tashin matattu, mutane ba za su yi aure ko su ba da aure ba; za su zama kamar mala’iku a sama. 31  Amma game da tashi daga matattu na waɗanda suka mutu ba ku karanta abin da Allah ya ce muku ba ne, 32  ‘Ni ne Allah na Ibrahim, Allah na Ishaku da kuma Allah na Yaƙub’*? Ai, shi ba Allah na matattu ba ne, shi Allah na masu rai ne.”
33 Da taro suka ji haka, sai suka yi mamakin koyarwarsa.
Doka mafi girma
(Markus 12.28-34; Luka 10.25-28)
34 Da jin Yesu ya ƙure Sadukiyawa, sai Farisiyawa suka tattaru. 35 Ɗaya daga cikinsu, wani masanin Doka, ya gwada shi da wannan tambaya. 36 “Malam, wace doka ce mafi girma a cikin dokoki?”
37 Yesu ya amsa ya ce, “ ‘Ka ƙaunaci Ubangiji Allahnka da dukan zuciyarka da dukan ranka da kuma dukan hankalinka.’ 38  Wannan, ita ce doka ta fari da kuma mafi girma. 39  Ta biye kuma kamar ta farkon take. ‘Ka ƙaunaci maƙwabcinka kamar kanka.’ 40  Dukan Doka da Annabawa suna rataya ne a kan waɗannan dokoki biyu.”
Kiristi, ɗan wane ne?
(Markus 12.35-37; Luka 20.41-44)
41 Yayinda Farisiyawa suke a tattare wuri ɗaya, sai Yesu ya tambaye su, 42  “Me kuke tsammani game da Kiristi? Ɗan wane ne shi?”
Suka amsa suka ce, “Ɗan Dawuda.”
43 Ya ce musu, “To, ta yaya Dawuda ya yi magana ta wurin Ruhu Mai Tsarki, ya kira shi ‘Ubangiji’? Gama ya ce,
44  “ ‘Ubangiji ya ce wa Ubangijina,
“Zauna a hannun damana,
sai na sa abokan gābanka
su zama matashin sawunka.” ’§
45  To, in Dawuda ya kira shi ‘Ubangiji,’ yaya zai zama ɗansa?” 46 Ba wanda ya iya tanka masa, daga wannan rana kuwa ba wanda ya sāke yin karambanin yin masa wata tambaya.
* 22:32 Fit 3.6 22:37 M Sh 6.5 22:39 Fir 19.18 § 22:44 Zab 110.1