5
Waƙar gonar inabi
Zan rera waƙa wa ƙaunataccena
waƙa game da gonar inabinsa.
Ƙaunataccena yana da gonar inabi
a gefen tudu mai dausayi.
Ya haƙa ƙasa ya kuma tsintsince duwatsun
ya shuka mata inabi mafi kyau.
Ya gina hasumiyar tsaro a cikinta
ya kuma shirya wurin matsin ruwan inabi.
Sa’an nan ya sa rai ga samun girbi mai kyau na inabin,
amma sai ga shi inabin ya ba da munanan ’ya’ya.
 
“Yanzu fa ku mazauna cikin Urushalima da mutanen Yahuda,
ku shari’anta tsakanina da gonar inabina.
Me kuma ya rage da za a yi wa gonar inabina
fiye da abin da na yi mata?
Da na nemi inabi masu kyau,
me ya sa ta ba da munana ’ya’ya?
Yanzu zan faɗa muku
abin da zan yi da gonar inabina.
Zan cire katangar da ta kewaye ta,
za tă kuwa lalace;
zan rushe bangonta,
za a kuwa tattake ta.
Zan mai da ita kango,
ba zan aske ta ba, ba kuwa zan nome ta ba,
sarƙaƙƙiya da ƙayayyuwa kuwa za su yi girma a can
Zan umarci gizagizai
kada su yi ruwan sama a kanta.”
 
Gonar inabin Ubangiji Maɗaukaki
ita ce gidan Isra’ila,
mutanen Yahuda kuma
su ne lambun farin cikinsa.
Yana kuma nema ganin gaskiya, amma sai ga zub da jini;
yana neman adalci, amma sai ga shi kukan azaba yake ji.
Kaito da hukunce-hukunce
Kaitonku ku waɗanda kuke ƙara wa kanku gidaje
kuke kuma haɗa gonaki da gonaki
har babu sauran filin da ya rage
ku kuma zauna ku kaɗai a ƙasar.
Ubangiji Maɗaukaki ya furta a kunnuwana,
“Tabbatacce manyan gidajen za su zama kango,
za a bar kyawawan gidajen nan ba kowa.
10 Kadada goma na gonar inabi zai ba da garwan ruwan inabi ɗaya kaɗai,
mudu guda na iri kuma zai ba da efa na hatsi guda kurum.”
 
11 Kaiton waɗanda suke tashi da sassafe
don su nufi wurin shaye-shaye,
waɗanda suke raba dare
har sai sun bugu da ruwan inabi.
12 Suna kaɗa garaya, da molaye a bukukkuwansu,
ganguna da busa da ruwan inabi,
amma ba su kula da ayyukan Ubangiji ba,
ba sa biyayya ga aikin hannuwansa.
13 Saboda haka mutanena za su yi zaman bauta
domin rashin fahimi;
manyan mutanensu za su mutu da yunwa
talakawansu kuma su mutu da ƙishirwa.
14 Saboda haka kabari ya fadada marmarinsa
ya kuma buɗe bakinsa babu iyaka;
cikinsa manyan mutanensu da talakawansu za su gangara
tare da dukan masu hayaniyarsu da masu murnansu.
15 Ta haka za a ƙasƙantar da mutum
kuma za a ƙasƙantar da ’yan adam,
za a ƙasƙanta da masu girman kai.
16 Amma Ubangiji Maɗaukaki zai sami ɗaukaka ta wurin aikata gaskiya,
kuma Allah mai tsarki zai nuna kansa ta wurin adalcinsa.
17 Sa’an nan tumaki za su yi kiwo kamar yadda suke yi a wurin kiwonsu;
raguna za su yi kiwo cikin abubuwa masu kyau da suka lalace.
 
18 Kaiton waɗanda suke jan zunubi da igiyar ruɗu,
da kuma mugunta da igiyoyin keken yaƙin,
19 waɗanda suke cewa, “Bari Allah yă gaggauta,
bari yă hanzarta aikinsa
don mu gani.
Bari yă iso,
bari shirin Mai Tsarkin nan na Isra’ila yă zo,
don mu sani.”
 
20 Kaiton waɗanda suke ce da mugunta nagarta
nagarta kuma mugunta,
waɗanda suke mai da duhu haske
haske kuma duhu,
waɗanda suke mai da ɗaci zaƙi
zaƙi kuma ɗaci.
 
21 Kaiton waɗanda suke tsammani suna da hikima
da kuma wayo a idonsu.
 
22 Kaiton waɗanda suke jarumawa a shan ruwan inabi
da gwanaye a haɗin abubuwan sha,
23 waɗanda suke ƙyale masu laifi don sun ba da cin hanci,
amma su hana a yi gaskiya wa marasa laifi.
24 Saboda haka kamar yadda harshen wuta yakan lashe kara
kuma kamar yadda busasshiyar ciyawa takan ƙone ƙurmus a cikin wuta,
haka saiwarsu za su ruɓa
iska kuma ta hura furanninsu kamar ƙura;
gama sun ƙi dokar Ubangiji Maɗaukaki
suka kuma ƙyale maganar Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
25 Saboda haka fushin Ubangiji ya yi ƙuna a kan mutanensa;
ya ɗaga hannunsa ya kuma buge su.
Duwatsu sun jijjigu,
gawawwaki kuwa suka zama kamar juji a tituna.
 
Saboda wannan duka, fushinsa bai huce ba,
bai kuwa janye hannunsa ba.
 
26 Ya ɗaga tuta don al’ummai masu nisa,
ya yi feɗuwa wa waɗanda suke a iyakar duniya.
Ga shi sun iso,
da sauri da kuma gaggawa!
27 Babu ko ɗayansu da ya gaji ko ya yi tuntuɓe,
babu ko ɗaya da ya yi gyangyaɗi ko barci;
babu abin ɗamarar da ya kunce a gindi,
ba igiyar takalmin da ta tsinke.
28 Kibiyoyinsu masu tsini ne,
an ɗaura dukan bakkunansu;
kofatan dawakansu sun yi kamar dutsen ƙanƙara,
ƙafafun keken yaƙinsu kamar guguwa ne.
29 Rurinsu ya yi kamar na zaki,
suna ruri kamar ’yan zakoki;
suna yin gurnani yayinda suke kamun abin da suke farauta
su ɗauke shi ba mai ƙwace shi.
30 A wannan rana za su yi ta ruri a kansa
kamar rurin teku.
Kuma in wani ya dubi ƙasar,
zai ga duhu da damuwa;
haske ma zai zama duhu ta wurin gizagizai.