6
A matsayinmu na abokan aikin Allah, muna roƙonku kada ku karɓi alherin Allah a banza. Gama ya ce,
“A lokacin samun alherina, na ji ka,
a ranar samun ceto kuma, na taimake ka.”*
Ina gaya muku, yanzu ne lokacin samun alherin Allah, yanzu ne ranar samun ceto.
Wahalolin Bulus
Ba ma sa abin tuntuɓe wa kowa, domin kada hidimarmu ta zama abin zargi. A maimakon haka, duk abin da muke yi, muna yin shi ne don mu nuna cewa mu masu hidimar Allah ne. Muna yin haka cikin jimrewa, da shan wahala, da shan wuya, har da shan masifu. Da shan dūka, da shan dauri, da yawan hargitsi, da yawan fama, da rashin barci, da kuma yunwa. Da cikin tsarki, da fahimta, da haƙuri, da kirki, da cikin Ruhu Mai Tsarki, da cikin ƙauna mai gaskiya, da cikin magana mai gaskiya, da kuma cikin ikon Allah. Muna riƙe da makaman adalci dama da hagu, ta wurin ɗaukaka da ƙasƙanci, da cikin ɓata suna, da kuma cikin yabo. Cikin faɗin gaskiya, an ɗauke mu masu ƙarya, mu sanannu ne, duk da haka an ɗauke mu kamar ba a san mu ba, muna mutuwa, duk da haka a raye muke, an ba mu horo, duk da haka ba a kashe mu ba, 10 cikin baƙin ciki, duk da haka kullum cikin murna muke. Cikin matalauta, duk da haka muna azurtar da mutane da yawa. Ba mu da kome, alhali kuwa kome namu ne.
11 Ya ku Korintiyawa, mun yi muku magana a sake, muka kuma saki zuciya da ku ƙwarai. 12 Ba mu ƙi nuna muku ƙaunarmu ba, sai dai ku kuka ƙi nuna mana. 13 A wannan zance kam, ina magana da ku kamar ’ya’yana, ku ma ku saki zuciya da mu.
Kada ku haɗa kai da marasa bi
14 Kada ku haɗa kai da marasa bi. Gama me ya haɗa adalci da mugunta? Ko kuwa me ya haɗa haske da duhu? 15 Wace daidaituwa ce tsakanin Kiristi da Iblis? Me ya haɗa mai bi da marar bi? 16 Wane alkawari ne tsakanin haikalin Allah da na gumaka? Gama mu haikalin Allah mai rai ne. Kamar yadda Allah ya ce,
“Zan zauna tare da su,
in yi tafiya a cikinsu,
zan zama Allahnsu,
su kuma za su zama mutanena.”
17 Saboda haka,
“Sai ku fito daga cikinsu,
ku keɓe kanku,
in ji Ubangiji.
Kada ku taɓa wani abu marar tsabta,
zan kuma karɓe ku.”
18 Kuma,
“Zan zama Uba a gare ku,
ku kuma za ku zama ’ya’yana, maza da mata,
in ji Ubangiji Maɗaukaki.”§
* 6:2 Ish 49.8 6:16 Fir 26.12; Irm 32.38; Ezk 37.27 6:17 Ish 52.11; Ezk 20.34,41 § 6:18 2Sam 7.14; 2Sam 7.8